NA TAFKA KUSKURE.


*Typing 1 january 2019*

*Chapter 1*

*Kaduna*

Da gudu wata mota 320 kirar toyota,ta shiga cikin wani private hospital mai

suna *S&S SAFANA SPECIALIST HOSPITAL*

Cikin Hanzari matar tabude motar tafito tayi cikin asibitin da gudu tana fadin"ku

taimakamin kada y'ata ta mutu ku taimaka min.." Nurses suka biyota aguje da

gadon daukan marasa lafiya,wata matashiyar budurwa ce aka fito da ita daga

cikin motan tareda wata dattijuwan mata,tsirtsetsen cikin keta wutsul wutsul

alamar yana gab da Fitowa Ihu take zabgawa iya karfinta tareda wasu maganganu

marasa ma'ana Da Hanzari suka gungurata sai labour room,Hajiya karima takalli

Momma tace"To ai sai kira d'anki shafaffe da mai ya taho ya girbi abunda ya

shuka" tafada dawani irin izgilanci,Momma tayi murmishi irin nata kan tace"Ayyah

Hajiya zai zo ba"a gabanki namai waya ba kan mufito,insha yanxu zai zo kila wani

abun ne ya tsaidashi"Tafada tana duban Hajiyar yamutsa fuska tayi zatayi magana

kenan Kamshin turaren azzaro visit yafara musu maraba ko ba'a fada musu ba

sunsan mamallakin kamshin.

Momma takara fadada fara'arta daidai lokacin da suka kariso maza biyu ne cikin

shigar suit Black and ash,rigar likitancine saye acikin su,Daya daga cikinsu ya

Karisa yana Fadin"Momma Har kun iso?

Cikin fara"a tace"mun iso Babana kashiga sun shiga da ita ciki"mtswssss tsakin

daya katsesu kenan suka juya atare suna kallon Hajiya kari datake zabgamusu

Harara,tace cikin kallon raini"Kaga mallam ba mgana zaka tsaya yi ba yata

nakeson nasan Halin data ke cike,tundazu anshiga da ita bawani labari"Tsam

dukkansu sukayi da rai kafin momma tayi karfin halin zame Hannunta tana

Fadin"Babana Hanzarta kashiga ga Halin da *SAKINATU* take ciki.

cikin takaici da bakin ciki ya juyo wow!! abunda na Furta kenan dogon bufullatani

mai cikar zati da kamala,yanada tsawon da dan kibam murjewa,dogon Hanci ya

mallaka tareda madaidaitan dan bakinsa pick kamar yana shafa janbaki

idanunsa,bakin gashin kansa yakwanta ye luf dashi,zagayayyen sajensa

yakaramasa kwarjini Fari ne tas mai jaja din nan abun burgewa goshinsa dauke da

tabon salla wanda yake kara masa kima a idon mutane,wani siririn gilashine mai

karama Fuskarsa kyau sanye a idanunsa,kallo daya zakamai ka fahimci tsayayyan

Namiji ne mai cikar zati da Haiba

*DR SAFWAN SALE SAFANA* kenan likitan daya kware gurin kula daduk abunda

yashafi mata wato gynea Doctor wanda ke tare dashi *DR TAHIR* ne Abokine kuma Amini garesa kuma abokin aikinsa dasuke aiki akarkashin asibitin shi Dr

safwan din.

Sai da ya isa kusa da ita yadan ramkwafa yace cikin dakakkiyar murya"Barka da

zuwa Haji......."

"wai shi na tambayeka"ta katseshi "yata nake bukatar jin Halin datake ciki anshiga

da ita tundazu naji shuru'"

takareshe fada tana wani jijjiga kamar wata yar daba,yadade tsugunne kafin

yamike cikin sanyin jiki,ya Nufi kofar labour room din yasa Hannu a handle din

kenan Wata murya cikin karaji da azaba yaji tana fadin

"Allah ya isa tsakani na dakai safwan,kayi min ciki kabarni da wahala,kacemin

Haihuwa babu wuya...Gashi....Gashi kabarni da wahala kai babu abunda kasani

sai ci kamar tuwo wlh bazan sake yadda dakai ba" cikin bakin ciki da Nadama

yasaki Hannun kofar ya juya ya Fara Tafiya duk suka bishi da kallo Hajiya kari tace

cikin daga murya"Kai safwan ina zaka ko bakajin ihun da sakina takeyi ne....".Ina

ko waiwayowa baiyiba saima kara sauri dayayi har yabace daga gurin.

Cikin Takaici Hajiya kari tadaga Hannu sama tana Fadin"wayyo ni karima nashga

uku"kan ta isa kusa Da momma tana Fadin"ke wata irin uwace kinaganin

wulakancin da d'anki yayi ma y'ata ammh kin gagara mai magana,saboda yagama

cin moriyar ganga ya dirkamata ciki ko"?

Takareshe Fada Tana zaremata ido,Momma tayi mirimishi daya zaman mata jiki

kam tayi magana Dr Tahir yarigata dacewa"Am....Hajiya kiyi Hakuri i promise u

sakina Zata Haihu lafy"yana gama fadar haka ya bude Kofar Labour Room din ya

Shiga.

Dakyar Dr safwan ya karisa office dinshi cikin kunan rai,toilet yafada yasakarma

kansa shower ko kayan jikinsa bai cireba Haka ruwan keta kwararamai yafi minti

talati ahaka so yake yarage radadin dake addabansa,Haka ya Fito ruwa na diga ta

ko'ina ajikinsa kan kujrerar dake office din yafada yana maida Numfashi.

Har abada baisan yaushe zai zama mutum a idanun sakina da mahaifiyarta

ba,baisan yaushe sakina da Mahaifiyarta zasu daina cimai mutumci ba shida

mahaifiyarsa ba,baisan sai yaushene zata darajasa ta kallesa amtsayin miji ba bai

sani ba,bai sani ba,yafada da karfi idanuwansa sun canza launi.

Yafi minti Hudu acikin wannan yanayin kafin ya sake Bude idanuwansa,gabadaya

Zuciyarsa ta gama cika da wani kunci kansa na sarawa lokaci daya jijiyoyin kansa

suka Dago,kansa ya Dafe lokaci daya yana Share Ruwan Dake Diga daga saman

kansa,kafin ya sake komawa ya jingina da jikin kujeran yana maida Numfashi a

jere kamar wanda yayi gudun tsere.

Runte idanunsa yayi yana ajiyar zuciya Lokaci daya yana Saukar Da Numfashi

Daga ganin yadda yake yi zaka fahimci yanayin Dayake ciki na bacin rai da dacin

Zuciya,idanuwansa ya bude yana bin Kofar shigowa da kallo lokaci Daya

Abubuwan da suka Faru abaya suka fara dawowamai daki daki kamar alokacin

Abun ke Faruwa tamkar yana kallo cikin magijin talabijin.

*Domin samun kasancewa cikin masu karanta Sanyaya biyu na Mr Bello da Matar

Naseer kan 350 duka biyun Single 1 kuma 200 vips kuma 400 ne Duka biyu kuma

600 ne Muna maraba daku masoyanmu Sai kunzo*

Commets,share,like and vote.... *02*

*SHEKARUN BAYA* " *DR SALE HABULE SAFANA* shine cikakken sunan Mahaifin Dr Safwan wanda

d'ane ga marigayi Justice Habule safana kafin Allah yamai Rasuwa,yayi

gwagwarmaya agwannati har kawo mutuwarsa

Dr sale habule safana Haifaffan garin safana ne dake jihar katsina,yana da

shekara bakwai aduniya Allah yadauki ran mahaifinsa,Mahaifiyarsa Hajiya Maryam

wacce suke kirada Hajiya mama ita tadinga kula da danta har yagirma,Yayi

sakandiri sch dinsa a barewa college dake zaria anan kuma yahadu da Aminsa

kabir kankia ganin sun fito daga jaha daya yasanya abotarsu tafi tafiya daidai.

Bayan sun kamallah makaranta suka Fada ABU ZARIA a inda Sale ke karantan

medicine shikuma kabir political science,ammh duk da haka suna Haduwa in

basuda lectures,Haka rayuwa tacigada da tafiya Har kabir ya kammala digirin

dinsa ya dora masters dinshi shikuma alokacin sale yatafi Bautar kasa.

Sale a garin adamawa yatafi bautar kasa kuma achan Allah yahadasa da

mahaifiyar Safwan Hadiza,Hadiza mahaifaffiyar Adamawa ce bafullatanan asali,

marainiya bata uwa ba uba sai kanin mahaifinta wanda yariketa mai suna Baffa

Sani Hadiz bata zurfafa lilimi ba iyakarta sakandiri ammh masaniya littafan

Addinin muslunci tana da ilimi fiye da tunanin mai karatu bai kammala bautar

kasa ba Allah ya kulla aurensu tareda jajircewan Hajiya mama.

Lokacin da'akayi bikin kabir kankia na kasar spain yaje yin phd dinsa,sai da

yadawo yaji amininsa yayi aure hakika ya tayasa murna kwarai matuka samun

mace irin Hadiza,Macece kyakyawa dogowa mai dogon Hanci da gashi,Bayan

kammala bautar kasarsa yafara aiki da Aminu kano,Yaso ya dauki iyalansa

sukoma kano da zama Hajiya mama taki amincewa dole yasa yabarsu nan safana

yana zuwa musu weeked

Bayan kammala karatun kabir kankia yafada siyasa kadangadan akuma lokacin

iyayensa suka masa aure da yar uwarsa Karimatu,karimatu tun tana karimar

shegiyar makirace,gata bawani kyau ba bakace mummuna ga gajarta,tun tana

yarinyanta take bala'in son auren mai kudi bata shiri da takala,gata da kyashi da

hassada ga bariki kala kala dan dai babu yadda zai yine yasa yahakura ya amshi

karima.

Yafara rike mukamin sakataren gwannatin janar katsina akuma lokacin Hadiza ta

haifi Safwan Hakika tunganin Farko da karima tama Hadiza taji ta tsaneta saboda

tafita kyau uwa uba hankali Natsuwa da tarbiya kai akomai tadarata shiyasa lokaci

guda kyashi ya shigeta,batawani sakarmata sai kiga tawani yamutse yamutse

kamar taga kashi shiyasa Hajiya mama ganin Farko tace"Kabiru ina karoro

wannnan ruwan yan Duniyan"kai tsaye agabanta mirmishi kawai yayi itakuma

karima tadago tana karema Hajiya kallo ta kasan ido.

safwan yazo cikin gata,badewa mahaifinsa ya tafi london karo karatu sai da ya

shekara uku kana yadawo lokacin yazama consultand,Safwan nada shekara biyar

iyayensa suka kaisa Nigeria turkish.tunda Hadiza ta haifi safwan bata kara

Haihuwa.

Haka dai Rayuwan ta cigada juyawa cikin nasara da kwanciyar Hankali lokacin da

Safwan ya kammala secondry sch dinsa lokacin Da Allah ya karbi ran Mahafinsa

hatsari yayi ahanyarsa tadawowa daga kano hakika matuwar Dr sale Habu safasa

ta girgiza yan'uwa da abokan arzika,Alhaji kabir yaji mutuwar Amininsa matuka sai

dai Hakuri

Hajiya da Hadiza wacce Safwan kekira da Momma suka dau dangana suka maida

Hankalinsu wurin kula da safwan,Lafawar abun yasa yadage kasar malesia zuwa

karatun medicine sai da ya shafe shekara sha kana yadawo lokacin yazama

cikakken likitan mata.

Shima din da Aminun kanon ya fara aikin kan chukun chukun bude asibitinsa ya

kammala da taimakon Dady Alhaji Kabir kanki wanda yake matsayin kwashinan

ilimi ta jahar katsina. Koda bude asibitin ya kammala baida na aiki da Aminu kano ba Saida ya tattaro

Su Hajiya suka dawo garin kaduna kana ya maida Hankalinsa kan asibintinsa,Dr

tahir Aminsane wanda suka Hadu a malesia course daya suka karanta,kuma yan

kasa daya shiyasa abotarsu tayi karfo Shiyasa bayan ya kammala asibitin ya

Nemosa don Atafi tare

Alhaji kabir bai yada iyalan Dr sale ba yana kokarin ziyartarsu in yasamu dama,duk

abunda suke bukatu tunkan suyi mgana yake kawo musu Hakika shi mutumin

kirkine sai dai Karima tanajin bakincikin abunda yake musu dan dai bayya zatayi

duk da yanxu ta mallakeshi sai abunda tace yakeyi

*WACECE SAKINATU*

SAKINAT KABIR KANKIA shine cikakken sunanta yace ga kwamishina Alhaji Kabir

kankia da Hajiya karima wacce ake kira Hajiya kari,yayansu hudu salmace babba

tana aure a portharcort wani controller ne sai laila dake auren wani dan kasuwa a

kano,sai Sakina daga ita sai Ummi.

Gabadaya ya"yan Hajiya kari laila da sakina,sune suka dauko halayyanta wanda

ma harsun gyasheta Salma ce da Ummi kadai suka fita dabam,dukkansu suna da

degree sakina business admistration takaranta Tana son taga tazama yar kasuwa

tana juya kudi ahannunta shiyasa tana dawo daga london bayan ta kammala

masters dinta Mahaifinta ya tallafamata,tafara odar kaya daga dubai zuwa Nigeria

irinsu dogayen riguna da takalma da jaka,kayan maza kai duk abunda yadanganci

sawa da kwalliya,cikin lokaci Allah yasa abun albarka cikin shekara biyu sakina ta

bunkasa tayi kudi tuni takeda dankara dankara shaguna a

kano,kaduna,katsina,zamfara,da gombe,Sakina boutique and costimetics,sakinat

shoes,etc.

Gabadaya Hajiy Kari bata kula da tarbiyan yaran ba kwamishina baya zama so

komai na Hannunta,shiyasa sakina tataso tun tana karama bata kunya ga raina na

gaba da ita bata da kunya ko kadan bata iya girmama nagabada da ita ba.

Sakina bawata kyakyawa bace ta azo agani bakace gajera ammh saboda shafen

nan na yaran zamani yasa takoma Fara,Wani gajeran hanci gareta tana da dan

tudun baki,kan nan kamar Hammatar dan iska kullum cikin gashin doki

take,tanason mu'amala da abun mai kyau duk da ita din bamai kyau bace,Sakina

bata kaunar talaka ko kadan shiyasa danginsu na kanki kowa yasanta da rainin

arziki shiyasa kaf suka fita harkansu sboda Hajiya kari inrin matan nan ne masu

kyashi arziki daga ita sai mjinta da yayanta.

Sakina yar gayuce ta karshe kullum cikin shigar alfarma zaka ganta,to tazo

kaduna duba shop dinta taji zazzabi ya rufeta tana Hanya shine tafada asibitin Dr

safwan ganin farko tamai yasace zuciyarta wanda dagashi har ita basusan juna

ba saboda kowa ba kasar nan yayi karatunsa ba,Ada ta dauka wasane sai da

takoma gida kana ta tabbatar da takamu da son Dr safwan,tayi kokarin

tayakiceshi ammh hakan ya faskara,abinciken da'aka matane tagano dane gun

Aminin Abbanta.

Da tama hajiya kari magnar kin bada goyan baya acewarta baida qualities din

auren yarta,ammh sakinat taki hakura,taci gaba da shisshigemai da kissa da

kisisina,Da hajiya taga yarta taki hakura yasa tashiga tafita har soyayyah mai zafi

ta kullu atsakaninsu,Lokacin da kwamishina yaji labari yayi matukar farinciki

dasamun suriki irin Dr safwan,kuma yakara zumunci tsakaninsa da amininsa duk

da baya raye.

Da Hajiya mama taji lbr tadaga tsalle tace bata yarda ba saboda sanin mugun

halin Hajiya kari ammh Dr safwan ya tubure dole tasa ta amince ita daman

momma batada matsala cikin lokaci kankanin komai ya kammallah Amarya tatare

a gidanshi dake kaduna,mai dauke da shashi biyu daya na momma da Hajiya daya

shine mallakin sakina

Sunkwashi amarci na tsawon wata guda kafin halayyan,Sakina sufara bayyana.

 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Contact Form