AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE )_
Murtuƙe fuska Banju ya yi ya ce
"Magaji! ba dawowa nayi ba"
"Na sani Banju! ba dawowa kayi ba,jarumar 'yata ce ta dawo da kai"
"Kaii Magaji! Kunceni! Idan ba haka ba yankin kwana ta koma toka! Dan kasan
wanene Banju! Bana da imani! Kasan karonmu da kai!" murmushi Baffa yayi yace
"Amma ni Magaji Bawa! ban gudu ba hakane Banju?" haɗe rai Banju yayi baffa ya
ci gaba da fadin
"A yanzu ko Magajiyata Aziza tsaf zan iya sakata kasheka! amma halin da ka
sakani yasa nake son kasheka da hannuna! ka fara ƙirga numfashinka daga yanzu
zuwa gobe" dariya Banju ya yi yace
"Ashe kuwa idan zaka kasheni zaka haɗa da 'yarka, karka manta gangar jiki daya
muke da ita" Baffa shima murmushi ya yi ya ce
"Duk makahon da kaji yace ayi wasan jifa yasan ya taka dutse bare mai ido kuma
kai ma kasan bakin rijiya ba wajan wasan makaho bane, a wannan tafiyar kaine
makahon inaji ka manta da cewa yanzu haka Azima na da aure ko? mijinta shine
zai fiddaka daga jikinta ni kuma na kawo karshenka ta yadda ba zaka kuma
dawowa ba, kisan farko da na kasheka ban so ba, amma a yanzu ne zan kau da
ka" wani ihu Banju ya yi yana son tsincewa, Baffa yace
"Aziza!" juyowa tayi ta kalli Baffa, Baffa ya mata alama da ido, ta gya ɗa masa kai
sannan tayi gaban Banju tana shirin sake kafar da shi, da karfi ya furta mata
"BAHULAAAAA!!" a kunne yana son tada Bahula dake jikin Aziza, wani ja da baya
Aziza tayi ta dafe saitin zuciyarta da kanta, ganin haka yasa Baffa jan Aziza da
sauri ya watsa mata wani farin hoda nan Aziza ta sulale zata faɗi Nawaz bai yi
kasa a guiwa ba ya tare matarsa, da yatsa daya Baffa ya do ki goshin Banju,
kamar anyi ruwa an dauke haka Banju ya tsaya cak, Mom cikin tashin hankali ta
kama hannun Aziza wacce take kwance a jikin Nawaz ta ce
"Dan Allah Baban Aziza kayi wani abu, Aziza ta sha wuya wlh! Duk wani masifa
kanta yake afkawa dan Allah tunda ga Azima a cire mata Banju ko Aziza ta huta,
me yasa baka kashesa yanzu ba?" cikin kunya Baffa yace sabida har yanzu yana
jikin Azima, idan na kashe Banju a yanzu Azima ma ta tafi!" nan Mom ta gane
abunda Baffa ke nufi, ta kalli Hajja wacce ke tsaye a gefe tayi lullubi tana duƙe da
kai, Mom ta ce
"Nawaz shiga da Aziza cikin gida, Maman Aziza? Dan Allah ki daina ɗaurewa kina
wannan kunyar taki, ki saki jiki ki rungumi yarki, an wuce wannan zamanin kunyar,
yarki ce fa? Karki cutar da kanki kina son jin dumin yarki amma ki ta rabewa, dan
Allah bana son haka, ai gwara ki ja ta a jiki kafin na dauketa" rasssss!! gaban Hajja
ya faɗi jin mom tace zata dauke Aziza, amma bata iya furta ko da uhum bane tabi
bayan Nawaz da ya shige da Aziza, mom ta ce
"Baban Aziza zamu yi magana" Baffa ya ce
"To madalla bismillah" gefe suka koma suka kebe, mom ta ce
"A ba wa Almazeen matarsa yau suyi mu'amala ta aure dan a kawo karshen
wannan masifan, karka ce zaka biyewa kunya, wajan ceton rai babu zan can
kunya, a nema masa inda za a kai masa matarsa, a gobe ka kashe Banju,idan kuma hakan ba zai yu ba to a bamu su mu koma birni idan yaso komai ya daidaita
a can Banjun ya fita sai a kashesa a can birni sai mu tafi tare da ku, amma ya ka
ce?"girgiza kai Baffa ya yi cikin sauri ya ce
"Maganar a bar yankin nan a shiga gari akwai matsala, ba zan boye miki ba,
Almazeenu zai fuskanci kalubale wajan kusantar Azima, Banju ya wuce duk
tunaninki , kuma bayan ya kusanceta zaiyi ciwo, ba lallai bane ku a cikin gari kuna
da maganguna irin tamu ta gargajiya, ga misali a kan Aziza haka tayi ta faman
ciwo sai da ku ka zo kafin ta samu furen huriri ta warke, a nan aka fara yaƙin a nan
kuma nake so a ƙarasata,bana so a kai muku masifa kuna zaman lafiya, burin
Banju kenan ya sake barin yankin nan,ni kuwa ba zan bar haka ta faru ba ta yardan
Allah, dazu bayan munyi sallar asuba maganar da Baffa Mandi da Arɗo suka min
kenan a ba wa Almazeenu Azima yau, akwai wani gida da Arɗo yasa aka zagaye a
can kusa da wajan gari, amma akwai tsirarakun fulani a wajan kawai dai gidan ne
shi daya, yanzu haka zamu tafi da shi Almazeenu din, kafin nan zan ba shi wasu
magunguna da rubutu su sha shi da Nawazu din, dan shi ma yana da bukatar haka
tunda miji ne ga Aziza" Mom ta ce
"To ba damuwa hakan ma yayi Allah ya iya mana" Baffa ya amsa da amin, mom ta
kira Nawaz da Almazeen tace musu su bi Baffa, Malam Yunusa kuma da kanin
mahaifinsu Nawaz Alhaji Karami suna tare dasu sarki chubado da mai unguwa ori
sai hira sukeyi ana shan damemmen fura da nono, gwanin sha'awa.
@@@@@
Gidan suka je, duk da gidan kara ne amma yadda aka shirya gidan ya burge
Almazeen, tarko Baffa ya saka a ciki da waje ta yadda ko Banju ya fice a jikin
Azima ba iya guduwa zaiyi ba.
Sannan Baffa ya ba wa su Almazeen da Nawaz wasu maganguna da rubutu yace
su sha, ya basu na kariya da na sha da na wanka da na gogawa dana murzawa
dana ɗorawa duka babu wanda bai basu ba, daga nan sukayi wani gida gaba
kaɗan da na inda aka ba wa Almazeen, Baffa yace
"Nawazu, kai ma a nan zaka zauna ka riƙe Aziza, dan a lokacin da abun da ke
jikinta zai fita zata iya shiga wani hali, zata iya fita hayyacinta, idan kuma ta
subuce zamu iya rasata na har abada dan babu abunda Banju ba zai yi ba" Nawaz
yace
"In sha Allah hakan ma ba zata faru ba Baffa, hakuri da gaskiya sune a sama,
zamuyi nasara a kan Banju bi'izinillahi ta'ala!" Baffa ya yi murmushi na jin dadin
samun sirkai kamarsu Nawaz da Almazeen, haka shi ma wannan gidan ma ya
saka matakan tsaro.
Wunin ranar kuwa Baffa bai zauna ba shiri yayi sosai ya koma asalin Garkuwa
Magaji Bawansa kyakkyawa fari dogon bafulatani mai dogon hanci da halin girma
da cikar zati da haiba.
Da daddare mom ita ce tayiwa Azima da Aziza komai,ita da Maman Beenah suka
raka Azima da Aziza, Almazeen wani irin kunya yakeji, hajja kuwa ta kasa fitowa a
bukka tana zaune tana tasbihi ga Allah, tana roƙon mai duka da ya fidda mata
yaranta lafiya, hakika ita kam ta ga jarabta.
Bayan an mikawa Almazeen Azima wacce take da ita da babu za a iya cewa duk
daya, sannan aka wuce aka kai wa Nawaz Aziza duk da shi ba wani abu bane zai
wakana a tsakaninsu.
Ko da su Mom suka koma itama ba kwanciya tayi ba, alwala tayi ta zauna ta
fuskanci gabas, Maman Beenah kuwa gadon kara ta haye tayi kwanciyarta dan
tace bacci takeji.
Baffa ma uban gayya bai ga ta zama ba balle ya rintsa dan kuwa a tsaye yake
kyam.
*AL-MAZEEEN DA BANJU AZIMA.* A bukka kuwa Almazeen zama ya yi ya kurawa Azima ido yana kallonta, shi bai ma
san ta ina zai fara ba, ya kwashi kusan mintuna talatin yana kallonta daga bisani
ya tashi ya ɗauro alwala ya yi sallah raka'a biyu, ya ciro wayarsa ya yi karatun
alkur'ani mai girma ya daga hannunsa sama yana adduoi sannan ya shafa ya miƙe
a hankali ya fara rage kayan jikinsa, wani magani da Baffa ya basa yace ya shafa a
jikinsa idan zai taba Azima, maganin ya shafa a hannunsa da dukkkan jikinsa,
yana tabata sai da ta girgiza,kwantar da ita yayi, Banju dake jikinta yana kallon
abunda ke faruwa ɗauresa kawai Baffa yayi, wani gurnani ya fara nan ya hau buge-
buge, Almazeen da iyakacin karfinsa ya fizgi kayan dake jikin Azima, nan dambe
ya kacame duk da banju yana daure amma ba shi ya hanasa kokarin yunkurin
kashe Almazeen ba shima Almazeen yaci albarkacin daure Banju da Baffa yayi
amma duk da haka yanaji a jikinsa, duk kalman da yazo bakin almazeen indai na
salati ne yin shi yake yi
,Banju bai gama sarewa ba sai da ya ga Almazeen ya yiwa Azima kaff da kayan
jikinta, yunkurin komawa maciji Banju yayi amma kafin ya fara hakan tuni
Almazeen ya karanto adduar saduwa ya fara kokarin shiga jikin Azima, wani
sarawa kansa yayi tare da wani wawan jiri dake shirin watsa shi waje daurewa yayi
ya riƙe kokaran gadon karan gam jikinsa na kyarma, nan Azima ta fara canzawa
tana zama wata halitta daban mai matukar ban tsoro da firgitarwa, kokarin zare
jikinsa yayi dan dama bai shigeta sosai ba, tunowa da maganar Baffa na cewa kar
ya kuskura ya kyale Azima har sai ta yi attisha sau uku dan duk hanyar da Banju
zai bi dan ya ga ya hana Almazeen kusantar Azima zaiyi, daga karshe kuma zai
kashesa ya kuma guduwa, tunowa da haka yasa Almazeen ya dage da iyakacin
karfinsa sakamakon b'ari da jikinsa ke yi ya shige Azima gabadaya, wani ihuu
Azima ta saka da karfi wanda sai da ya karaɗe gefe da kewayen inda suke, ta
shaƙo wuyan Almazeen wanda shi kadai yasan abunda yakeji kamar ana zare
ransa haka yakeji tsananin azaba dan harta fatarsa ji yakeyi kamar ana soya masa
shi, sake damƙar kafaɗun Almazeen Azima tayi ta dage ta saki wani attishawa
mai karfin gaske dan kuwa an karya makarin Banju tunda Almazeen ya afka
cikinta, tana yin attishawa na ɗaya tayi na biyu, na ukun ne nan wani guɗa ya hau
tashi, tana attishawar Banju wanda ya yi tsalle ya fice ta baki da hancin Azima,
ƙauuuuu! Azima taji yayinda ta wani firgita tana jan wani numfashi da iskar
duniya,da nauyin kai ta hau ware ido da kyar jin idon kamar an liƙe mata su, tana ji
tamkar yau ne uwarta ta haifeta, tana gama buɗe ido mutum ta hanga a saman
kanta, Almazeen wanda yake gaff da sumewa yana ganin ta bude ido a hankali ya
sauke bakinsa saitin kunnenta cikin mayuwacin hali da kyar ya furta
"Alhamdulillah! Wlcm back my dear wife, am so happy, u are back! i promise that i
wouldn't let any harm attack u, i will sacrifice my life to u, cox I luv u, am really luv
u, i fell in luv with u Azima! pls don't leave me alone" Almazeen na faɗi ya hau
kokarin zare jikinsa daga na Azima, a lokacin Azima taji wani mugun raɗaɗi ta
kasanta hakan ne yasa taja wani numfashin mai cike da azaba, a tare suka suma.
Banju dake tsaye yana
kallon Almazeen wanda yake son kashesa dan ya lashi takwabin sai ya kashe
Almazeen, amma inaaa ya kasa kusantar almazeen balle ya kashesa kasancewar
Almzeen mutum ne mai riƙo da ibada baya sanya.
*NAWAZ DA AZIZA.*
Sadda aka raka Aziza tsayuwa tayi a bakin bukkar taki karasowa, Nawaz na zaune
yana danna wayarsa da tun shigowarsu garin babu network ko ɗigo, ɗaga ido ya yi
ya kalleta ya ga jikinta sai rawa yakeyi, da alama tsorata tayi, a hankali ya tashi
yaje gabanta bata ma sani ba tayi zurfi a tunani, ji tayi an kama hannunta, a firgice
ta dago idonta ya haɗe da na Nawaz, ganin duk ta taburce yasa Nawaz rausaya
kai yace
"Ya haka? Jaruma a waje, matsoraciya a gabana?" ya faɗa yana matsota sosai, ja
da baya tayi tana shirin ficewa yasa hannu ya jata ta shige jiki jikinta, yasa hannunsa duka biyu ya kewayeta ta kasa kwacewa ya ce
"Ko za a watsar dani ne?" nan ma bata masa magana ba, ya ce
"Idan baki min magana ba, zan cinye bakinki" mamaki ne ya kama Aziza, oh dama
haka Nawaz yake? take tambayar kanta, bata gama yankewa ba sai da taji ya
dauketa ya ajiyeta a saman gadon kara yana shirin kwanciya a kanta tayi saurin
miƙewa zunbur tana fadin
"Sorry Hamma" murmushi ya yi a boye, ya ce
"To matso kusa dani, kin san Baffa yace na rikeki da kyau dan haka matso" ya faɗa
yana ware mata hannu alaman ta shigo cikin jikinsa, ganin yadda ya sauya fuska
ba alaman wasa yasa ta matso a hankali ta shige jikinsa ta kifa kanta a ƙirjinsa,
yasa hannu ya rungumeta da kyau yana son fassara me zuciyarsa takeji game da
Aziza.
A lokacin da Almazeen suka fara dambatuwa da Banju, a lokacin Aziza na kwance
a jikin Nawaz, lokaci daya kamar an zabureta haka ta miƙe, cikin hanzari Nawaz ya
fizgota ya maidata jikinsa ya matseta dan ya tuno da maganar Baffa da yake cewa
idan Aziza ta subuce za a iya rasata shiyasa ya kara matseta sosai a jikinsa, ihu
Aziza ta saka jin fatar jikinta na sabulewa, saurin ture Nawaz tayi ta koma gefe
tana ƙanƙame jikinta, fuskarta ne ta ji yana b'anb'arewa, hannu biyu tasa tana tare
fuskarta tare da ihu, ganin halin da take ciki yasa Nawaz saurin tashi zai zo gareta,
nan yabga masifa, daga ƙugunta abunda ya yi sama ta zama macijiya fara sol sai
kyalli take yi, sak irin wanda yake gani a mafarkinsa, hannu ta miƙa masa cikin
azaba tana fadin
"Help me plss! ka taimakeni Hamma Nawaz!" ta faɗa siffar jikinta na ƙasa na
haurawa zata zama macijiyar gabadaya, da saurin Nawaz ya rintse ido yaje ya
rungumeta ƙaƙam! Yana rungumarta ta tsaya a haka, a lokacin da Banju zai fita a
jikin Azima itama Aziza taci azaba dan nan suka hau gwada karfi da Nawaz,
hakika shima ya jikata, dan kuwa sadda abun zai fita gani ya yi wani farin abu shi
ba dutse ba shi ba tsuntsu ba ya fice ta goshin Aziza, yana fita numfashinta ya
tsaya cak yayinda ta koma mutum, haka Nawaz ya zauna riƙe da ita a jikinsa,
gab'ob'insa na masa ciwo sosai, har asuba.
Sanyin asuba ne ya fara farkar da Almazeen wanda da kyar yake iya buɗe ido
sabida nauyin da suka masa, ya jima a haka kafin da layi ya tashi ya janyo kayansa
ya saka, ya rufawa Azima jikinta, ya koma ya kwanta a gefenta yana sauke huci
mai zafi.
Baffa suna idar da sallar asuba Arɗo yace su je a duba yaran nan.
Mom aka kira dan da ita za aje Hajja ta ƙi fitowa ƙememe.
Suna zuwa gidan Hajja zata shiga da saurin Baffa ya dakatar da ita ya hanata
shiga, yace tana shiga Banju zai iya kasheta dan shi yanzu duk wanda ya samu zai
kashe ne" Baffa ne ya fara shiga cike da yarda da kansa sabida ya yi imani da
Allah ya yi riƙo da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam,duk wanda ya yi riƙo
dasu baya da fargaba a kan kowa, yana shiga kuwa Banju dake neman hanyar
guduwa a gidan tun daren jiya ya kasa sabida Baffa ya ɗaure ko ina da ina, suna
ido huɗu Baffa ya daga takwabi, Banju yace
"Magaji a gwabza idan ba tsoro! karka kasheni sai mun gwabza!" Baffa ya yi
murmushi yace idan ka so haka"
"Zan so! amma ka ajiye takwabi" Baffa ya ce
"Ba daga yanzu zamu fara ba, kafin nan ga wannan" Baffa na faɗi ya wurgawa
Banju wani igiya nan ya daure Banju ya fito da shi, yana fitowa da shi ita kam mom
bata iya daga ido ta kalli Banju ba, dan tace mugun ji da mugun gani Allah ya
rabamu dasu, Baffa na cewa zata iya shiga da sauri ta wuce shi kuma ya wuce da
Banju, mom na shiga ta samesu a yashe, Azima ta jijjiga sannan ta taba Almazeen
wanda jikinsa ke rawa alaman ciwo jikinsa zafi raɗauu kamar wuta, na Azima ma
akwai zafi amma na Almazeen ya fi nata, babu wani taimako da zata iya masa,
amma zata iya taimakawa Azima, dan haka ta fito ta haɗa ƙirare ta tafasa ruwan zafi, kafin ruwan ya gama sai ga jikan Ardo Sanda ya kawo wasu magunguna yace
Baffa yace idan su Hamma Almazeen da Azima zasuyi wanka a zuba musu shi a
ruwan wankan suyi wanka da shi, wannan kuma su sha, sannan a ba wa Hamma
Mazeen wannan,wannan kuma a ba wa Azima" mom ta karba tana masa
sannunsa da aika.
Mom da kanta ta taimakawa Azima tanuna mata yadda zatayi wankan tsarki,
sannan tayiwa mata wanka haka,ita dai Azima wani iri take jin kanta, riƙota mom
tayi suka shiga bukkar har yanzu Almazeen ya kasa motsi koda da yatsarsa daya
ne, taimakawa Almazeen mom tayo shima ya yi wanka ya yi sallah a zaune ya sha
magungunan da Baffa ya bada a ba shi daga nan ya hau bacci,itama Azima
maganin ta sha ta hau bacci, haka ma Aziza wanda aka aika aka ba wa Nawaz
yasha ita ma ya bata ta sha duk suka buge suka hau bacci.
Can wajan dandalin yanki Baffa yaje ya daure Banju, ko kaɗan Banju baida kyawun
halitta gani, ga girma katam da shi tamkar basamude ga baƙi fiye da misali, kai
babu ta yadda za a sunfanta zubin halittan Banju.
Bayan Baffa ya daure Banju yasa maga isar da sakon yankin kwana a kan ya
rubuta wasika yayi aike sauran yankuna ana gayyatar su izuwa kallon fafatawa a
tsakanin aljani Banju da Baffa bisa umarnin gayyatar sarkin yankin kwana wato
sarki chubaɗo, kamar irinsu yankin ja'i da yankin tudu da yankin ja'o da yankin
gangare, da yankin shani, da dai sauran yankuna.
Sadda wasika ta iskesu sun sha mamaki, kai wannan ai babban fafatawa ne a
tsakanin Magaji bawa da Maciji Banju, wanda ya yi b'arna da ta'adi a yankin
kwana, wanda ya kashe shahararrun masu kama macizai irinsu jarman macizai
dasu Innu maciji, da iro mai maganin macizai da dai sauransu, hakika duk
yankuna sun amince zasu zo ganin wannan fafatawar tsakanin mutum da
aljan,duk da wannan ba sabon abu bane a wajan Garkuwan Kwana Magaji Bawa
Arɗo.
Mom ce ta cewa Baffa dan Allah ya taimaka ya raba Aziza da Bahula ta koma
asalin cikakkiyar mutun ɗinta ta huta gaba daya, Baffa ya yi murmushi ya ce
wannan ba wata matsala ba ce, suka je gidan har zuwa yanzu suna bacci, goshin
Aziza Baffa ya riƙe ya rintse ido, attishawa Aziza tayi sannan ta fara hamma, wani
farin abu ne ya fito ta bakinta, a hankali farin abun ya koma kamar farin hayaki
haka, daga nan abun ya zama mutum wanda ake mata kallon dishi-dishi, Baffa ne
kawai yake iya ganinta dan kuwa mom ba ganinta take yi ba, kallon Baffa Bahula
tayi tana girgiza kai hawaye na zuba a idonta dan tasan Baffa kashe mata Yayanta
Banju zaiyi dan tasan ko a wasa Yayanta Banju ba zai haɗa karfinsa da kwatan
karfin da Magaji ke da shi ba,kawai dai a mugunta ne baya da lamba ta biyu, dukar
da kai Baffa yayi, daga haka Bahula ta b'ace, muryan mom Baffa yaji tana magana
"Baban Aziza? Yanzu shikenan sun warke babu wata matsala ko?"
"In sha Allahu, sun warke, amma wanda ba yanzu zaiji sauki ba wanda shi ba mu
san a ya zai farka ba shine Almazeenu, amma harta Azima zata farka lafiya
lau,kuma idan ta farka za a gaya mata gaskiyar abunda ya faru kar a boye mata
duk da abun da suka faru zata iya gani duk da ta kasance a sume amma zata iya
gani kamar mutum mai bacci yana mafarki sabida sun rayu a jiki daya da
Banju,jikin ma kuma nata ne, zata tuna komai kuma zata gane komai shiyasa za a
gaya mata sabida rashim gaya mata zai iya haifar mata da wani matsala, mom ta
gya ɗa kai tana mai tausayawa Almazeen.
Basu suka farka ba sai lokacin sallar azahar, wani ɗauuuu!! Aziza taji a kunnenta
da ta farka, zata fadi da saurin Nawaz ya riƙeta, wanda shima yanzu baya jin
komai ciwon jikin nasa ya tafi
"Kina lafiya?" Aziza ta gya ɗa kai tana gyara tsayuwarta, zuwa can ta ce
"Azima? yar uwata?" ta faɗa zata fice da sauri Nawaz ya rikota yace suyi sallah
kafin su tafi, sallan kuwa suka gabatar shi ya jasu sannan suka fita sukayi gidan da Almzeen da Azima suke, mom ma tana gidan tana kula da Almazeen wanda a
zaune ma ya ƙara gabatar da sallah, Azima kuwa tunda ta farka har tayi sallah
karo na farko a rayuwarta, bata furta ko da uffan bane kallo kawai take bin mutane
da shi abubuwa suna dawo mata kamar a mafarki haka take tariyowa, tana zaune
a kan sallayar kaba su Nawaz da Aziza suka shigo da sallama, Aziza tana ganin
Azima a kan sallaya tasa kukan farinciki tana fadin
"Azima?" daidai lokacin su Inna wuro da su Yawuro har ma da Hajja dasu Baffa
suka shigo, juyowa Azima tayi tana binsu da kallo, ganin Aziza yasa ta ce
"Aziza?" wani kuka Aziza tasa ta ƙaraso da sauri suka rungume juna ƙaƙam
"Me ya faru Aziza?" Azima ta tambaya cikin sheshsheƙar kuka
" zan gaya miki" cewar Arɗo, nan ya hau yiwa Azima bayani dalla-dalla tun fara
kisa da yaƙi da komai da barin yankin kwana har izuwa yanzu, wani kwalalo idanu
waje Azima tayi ta hau girgiza kai tana fadin
"Ni....ni....ni....ban.....ban....ban...kashe....kowa....ba.....Baffa.......bana....da niyyar
kasheka...Hajja ban miki rashin kunya ba.....Aziza...banyi faɗa dake ba.....dan Allah
kuyi hakuri..... Ban kashe kowa....ba..." duk Azima ta bi ta ruɗe mom ta jata a jiki ta
ringume tace
"Mun sani Azima,mun san cewa jinin Magaji da Jamila ba zata aikata hakan ba,
kwantar da hankalinki, ba ki kashe kowa ba,mugun nan azzalumin aljani Banju
shine ya kashe" ɗago daga jikin mom tayi tana kan ci gaba da kuka, duk da zafi da
ciwo da ƙasanta ke mata ba shi ya hanata tashi da gudu ta shige jikin hajja da
kuka ba, itama Hajja kukan takeyi, dagowa tayi ta kalli Baffa ta hau girgiza kai da
hannu tana fadin