Daurin boye

*DAURIN BOYE* 

*NA*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*

HASKE WRITERS ASSO

(home of expert and perfect writers)

Tsaye yake cikin tafkekan dakin taron a gaban wani hamshaqin teburi wanda yake

dauke da aqalla ma'aikata kimanin mutuk arba'in,hannunsa guda dafe yake da

gaban teburin yayin da daya hannun yaketa wulwulgashi cike da gwanancewa duk

da baisan yana yi ba,da alama bayanin da yakewa ma'aikatan da suka bashi

dukkan nutsuwarsu ya dauki zafi,lokaci lokaci yana daga daya hannun nasa dake

dafe da teburin yana duba agogon hannunsa,wannan kadai ya isa ya nuna maka

mutum ne mai kiyaye lokaci da kuma alfanunsa.

"Is there any problem?...." Ya qarashe jimlar tasa ta qarshe yana duban fuskokin

ma'aikatan,saidai kowanne ya gamsu girgiza kai suka dinga yi daya bayan

daya,ganin haka ya sanya shi ya soma tattare kayanshi dake saman teburin tare

da bada umarnin a rufe taron da addu'a kaman yadda yake a qa'idarsa.

Shine mutum na farko da ya soma fita,shahid ya rufa masa baya suna magana

qasa qasa,a bakin hall din daya daga cikin mutanen dake tsaye a wajen ya karbi

kayan hannunsa sannan yabi bayansa har cikin elevetor wadda bata saukesu ko

ina ba sai hawan qarshe na kamfanin inda office dinsa yake.

Mahmoud ne kawai zaune cikin office din ya tasa computer a gaba da alamu wani

aiki yake ragewa mai muhimmanci Hannu mahmoud ya baiwa shahid suka gaisa

cike da alamun cikakkiyar sanayya a tsakaninsu bayan security din dake riqe da

kayan khaliphan ya aje ya fice,yayin da khalipha ya wuce kai tsaye bakin freezer ya

dauki ruwa ya sha bayan ya rage suit din jikinsa kana ya shige toilet,alwala ya

daura sannan ya dawo cikin office din ya tadda shahid da mahmoud suna

hira,wadda fiye da rabinta abinda ya shafi kasuwancinsu ne,daya daga cikin

wayayoyinshi wadda ke dauke da lambobin dukkan mutanen daya baiwa

muhimmanci a rayuwarsa lambarsu ke ciki,kai tsaye ya nufi bakin daya daga cikin

windows din dake cikin dakin office din wanda kai tsaye zaka iya kiransu da qofa

saboda kadan ne ya rage basu kai girman qofar ba,saidai glass ne zalla a jiki

wanda hakan zai baka damar gano ainihin farfajiyar companyn daga sama har

qasa.

Bugu biyu aka daga wayar,ya sauke ajiyar zuciya sallamar matar na ratsa

kunnensa,cikin sanyin murya kaman yadda halittar muryarshi take ya amsa

sallamar sannan yace"Anni...barka da warhaka"

"Barka kadai khalipha,kun fito daga taron ne?"

"Mun fito ammi,saidai aci gaba da yi mana addu'a Allah yasa mu dace"

"Ubangiji ya dafa,ya shiga lamarinku,ya zama jagora a gareku,ya albarkaci

rayuwarku". Cike da jin dadi yaketa amsawa da ameen,idanunsa lumshe yana

shafa qirjinsa yana jin zuciyaraa wasai

"Ya jikin anni?,kinsha maganinki na rana,naga lokaci yayi"murmushi ta saki cike da

qaunar yaron nata

"Khalipha kenan baka gajiya?,kaman ba awannin da suka shude muka gama waya

da kai ba,jiki alhamdulillah,magani kuma ina gama sha kiranka ya shigo"cikin

murmushi ya amsa

"Ya za'ayi na gaji da jinki anni....Allah ya qara miki lafiya mai dorewa". "Allahumma amin khalipha,Allah yayi albarka"

"Ameen anni...sai na dawo"

"Allah ya tsare" ta sake ambata cikin nuna kulawa da qauna,ya amsa sannan ya

kashe wayar yana murmushi,abubuwa da yawa na dawowa cikin kwanyarsa game

da annin tasa,zai iya cewa baiga uwa irin tashi ba,kuma baya zaton za'a

samu,anninsa da taban ce ko cikin halittun ubangiji,da wannan zancan zucin ya

qaraso inda su mahmoud suke.

Zaune yake gaban annin tashi cikin shigar qananun kaya na t shirt da

trouser,qafafunshi tanqwashe gabanshi kuma plate ne wanda ke dauke da tuwon

shinkafa miyar water leaf da ogu wadda ta wadata da ganda busashshen kifi da

kuma tsokar nama,a nutse yake cin abinci gefe guda suna hira da anni,hirar dake

nuna tsantsar shaquwa dake tsakaninsu,kallo daya zaka yi musu ka tabbatarwa

kanka lallai akwai saboda da shaquwa mai qafi tsakaninsu

"Khalipha..." Ta ambata a hankali wanda hakan yasa ya dago kanshi yana dubanta

sannan ya amsa

"Wai sau yaushe zan daina jiran ganin zuwam surukata?" Murmushi ne ya subuce

masa,sai ya aje cokalin hannunsa ya fasa kai lomar da yayi niya,cikin kulawa da

qauna yake dubanta sannan yace

"Kwanan nan anni,karki damu....addu'arki nake buqata kawai...ina son na kawo

miki surukar da zata kulamin dake,surukar da zata daukeki a matsayin

uwa....surukar da zakiji dadin zama da ita fiye dani yadda zanji" murmushi ya

subuce mata,sai ta kada kai tana dubanshi

"Allah ya baka mace ya gari wadda zata zame maka majingina.....amma banda

abin khalipha kana tunanin akwai irin wannan surukan yanzu?" Ta qarashe

managanar tana dariya qasa qasa,don har ga Allah bata dauki burinta ta cillashi

har haka ba,kullum dai addu'arta Allah ya bashi wadda zata soshi tsakani da

Allah,nagartacciyar matar aure,dan marairaicewa yayi kadan sannan yace

"Anni,kin sha gayamin ba'a fidda rai da rahamar Allah"

Kai ta jinjina cike da gamsuwa tace"wannan haka yake,ubangiji ya maka zabi ja

gari"

"Ameen" ya amsa yana daukar cokalinsa dinci gaba da cin abincinsa sannan yace

"Cikin sati na gaba haidar zai dawo gida hutu" murmushi tayi kaman ko yaushe

"Sun kammala jarabawar kenan"

"Eh sun samu hutu na wata biyu"

"Allah ya kai mana rai"

"Ameen" ya amsa yana daukar cup din daya cika da ruwa ya soma sha.

Da sauri sauri take tafiya hadi da duba agogon hannunta,qarfe tara da rabi na safe

dai dai,mintuna talatin zata qara ta makara wanda hakan dai dai yake da rasa

lacture dinta har na tsahon awa biyu.

Turus tayi gabanta na dan dokawa ganin asma'u zaune dafa'an cikin falon sanye

da kayan barci wanda hakan ke nuna ko wanka bata yi ba bare a kai ga shirin

fita,hannunta daya riqe da cup na tea tana kurba a hankali,daya hannun kuma

wayarta ce samfurin iphone 8 take latsawa,jikinta sanyaye ta qaraso gefanta ta

tsaya

"Ashe baki shirya ba anty asma'u?" Sai data shaqi iska kafin ta amsa

"Eh....sai eleven"

"Gashi goma lacturer din yake shiga..." Ta fada adamuwance,saboda daddy yana

gidan,kusan yasan lokutan fita lactures dinsu daya ne,tare suke fita su kuma dawo

tare a iya saninsa kenan,idanu ta daga ta kalleta ta watsa mata wani kallo

"Naga alamun raini na son soma shiga tsakaninmu aysha duk don saboda sharing

abun hawa da muke ko...to ki shiga taitayinki,ke kanki kinsan wutsiyar raqumi tayi

nesa da qasa,banda game game irin ja daddy da sunan zumunci saidai ki dinga

hangoni ta cikin glass,to banson zura kai in zaki wuce kije ki hau abun hawa na

haya ki wuce,dama dashi kika fi dacewa kuma dashi kika saba" tana kaiwa nan ta

maqala earpiece a kunnenta da alama kira ne ya shigo mata zata amsa.

A kasalance take takawa a harabar gidan,zuciyarta cike fal da tunani,tana

tsammanin kyautatawa na sanyawa kaso mutum koda baka sonshi,saidai ta

gefan asma'u sam ba haka bane,mommy kuwa har yau ta kasa fahimtar a wanne

aji take?,banbancin rayuwar data baro da wannan baya wuce sauyin muhalli,sutura

da ilimi data samu ba,amma baya ga haka zata iya kiran yanayin da SAMMAKAL a

wajenta

"A'ah,ina zaki a qafa aishatu?" Ta tsinkayi muryar daddy dake fitowa daga babban

falonshi da yake ganawa da baqinsa,wanda sam bata lura da shi ba saboda zurfin

tunanin da tayi,cikin hikima tayi qoqarin saisaita yanayinta,ta qaraso cike da

girmamawa

"Ina kwana daddy..." Ta soma da gaisheshi,don yau duka basu samu damar

haduwa ba,kasancewar jiya wajen goma na dare ya dawo qasar,ya kuma buqaci

mommy ta tasota saidai tanajin sa'adda da tace masa ai ayshan tayi bacci,bayan

idanunta biyu a sannan litattafanta ne a gabanta take dubawa,har lokacin data

shiga dakin asma'u ta tadata kan ta fito daddynsu ya dawo amma asma'un tayi

qememe tace ta gaji sa gaisa gobe,haka mommyn ta fito tace masa itama din tayi

bacci

"Ina zaki aysha?" Ya sake jeho mata tambayar bayan sun gama gaisawa,bata da

wata qarya da zata masa don kare asma'un wannan karon,saboda haka kai tsaye

tace

"Makaranta" agogon wayarsa ya duba sannan yace

"Ina asma'un.....ina kuma drivern naku?"kanta ta duqar qasa sannan tace

" yau akwai banbancin lokacin fitar namu ne"

Kai ya jinjina,tun da can shi ba mutum bane mai yawan sanya ido da takura

ba,hakan ya sanya abubuwa da dama kan gudana cikin gidan ayi musu

kwaskwarima a sauya musu salo a bashi a haka ya karba ba tare da ya sani ba.

Dai dai sannan usama drivansa ya turo get din gidan ya shigo,saboda ga

tsammaninsa a sannan zasu tafin,hakan ya sanya daddyn ya sallameta bayan ya

miqa mata sabbin 'yan dubu dubu guda biyar da sukayi saura a hannunsa wanda

da alama ya gama sallamar masu neman taimako ne wadan nan suka rage,tasan

baya kyauta a dawo masa da ita hakan ya sanya tasa hannu biyu ta amsa tana

jero masa godiya.

Ko cikin motar tunanin karamci irin na daddyn take,har abada kuma har ta mutu

ba zata taba manta alkhairinsa da karamcinsa gareta ba,qarar wayar usama ta

dawo da ita hayyacinta,daga jin yadda yake amsa wayar cikin daburcewa tasan

akwai magana

"Kiyi haquri ranki ya dade,yanzu zan ajeta na dawo,na dauka yau bazaki fita

bane...kiyi haquri" kalmar yayita maimaitawa,saidai hakan bai hana asma'u yi

masa tas ba harda alakoron zagi ta kuma katse wayar

"Kaga....ajjiyeni usama kaje ka daukota saina qarasa wani abun hawan" yana

bala'in ganin qimar ayshan saboda yadda take girmamashi tamkar yayanta,hakan

ya sanya yace

"Barshi kawai na qarasa dake aishatu,koda na ajekin ma na koma daukota ba tsira

zanyi ba" kai ta kada

"Ka ajenin babu komai...laifin ai zai ragu idan kace mata ajjiyeni kayi ba kamar ka

kaini ka dawo ba" haka ya gangara gefan titi bada son ransa ba ya ajeta ya juya ya

koma,ta tsaida adaidaita sahu ya qarasa da ita,idan da sabo ta jima da sabawa da

halayen asma'u,ta haddacesu tsaf,shi yasa ba komai ke bata ranta ba.

*mrs muhammad ce*











Post a Comment

Previous Post Next Post

Contact Form